Ingantaccen Hanyar Samun Sauki Gurin Nakuda

Tabbas mata da yawa sukan sha wahala sosai idan watan haihuwarsu ya kama domin Allah kadai ya san cikin irin yanayin da suke shiga. Wannan shafin mai albarka, ya kawo maku wata fa’ida wacce tabbas mun tabbatar da ingancin ta idan aka jaraba in sha Allah za a dace duk mata mace mai shan wahalar nakuda to ta samu Zuma mai kyau kaman cikin Kofi ko cokali 24 ta shanye a take..., Sannan a samu wani zumar a zuba ruwan zafi a ciki tana shan shi da zafi wannan zai taimaka wajen juya yaro in sha Allah. Hakan yama fi ruwan nakuda karfi, Sai dai kuma in Allah bai yi fitar yaron ba a lokacin amma inba haka ba a take yaron zai fito in sha Allahu. Shi ya sa yana da kyau sosai da zarar cikin mace ya kai wata 7 ta dinga tafasa ‘ya’yan hulba tana zama a ciki kullum sau daya in ya shiga wata 9 ta dinga yi safe da yamma. Hakan zai taimaka sosai wajen bude kofofin aihuwa kuma da wuya mace ta karu a lokacin aihuwa. Kuma mace za ta samu garin hulba ta kwaba da Zuma tana shan cokali biyu safe da yamma, in sha Allahu za ta samu sauki sosai wajen aihuwa amma kada mace mai ciki ta yi amfani da hulba har sai cikin ya tsufa ma’ana lokacin nakuda saboda hulba tana zubar da yaron ciki. Allah ya sa mu dace dan Allah duk wanda ya karanta to ya yi kokari ya sanar wa yan’uwa mata saboda a samu saukin nakuda sannan kuma a samu saukin fidar yaro daga cikin mahaifa.
                               
BuGu Da Kari:




MAGANIN NAKUDA
Idan cikinki yakai wata 7 anaso duk bayan sallar magriba ki ringa karanta
1""suratul falaq 41
2""suratul mass 41
Kina tofawa a ruwa kinasha kullum
2""kisamu dabino kullum anaso kiringa cin guda 3 ko 7yana matukar karawa mai ciki lapiya kuma yanasa ta haypo yaro mai hakuri
3""idan cikinki ya kai watan haihuwa anaso kisa arubuta miki
Ayatul kursiyu kafa 33 tare da aya ta 10cikin suratul khahfi kafa 33shima
Ki ajiye da zarar kinji alamun haihuwa ki dauka kicinye
4"""anaso mai nakuda taci danyen dabino guda 7alokacin da take nakuda domin dashi Allah s.w.a yayiwa sayida Maryam wahayi alokacin da take tsaka da nakudar Annabi Isah a.s kunga kuwa da akwai abinda yafishi muhimmanci ga mai nakuda da anyi mata wahayinsa
Allah Dan girmanka ka baiwa mata haihuwa mai sauki Dan sirrin dake cikin suratul fatiha ameen
SIRRIN RUWAN ZAM ZAM
Wannan ruwa dashi aka wanke zuciyar ANNABI SAW, a lokacin yana dan shekara hudu, a wajan Halimatus- Sadiya, da kuma lokacin tafiya Isra'i
MANZON ALLAH SAW YAce: Ruwan zamzam, (zaa sami biyan bukata da niyar ) da aka sha. Sahihu ibn Majah.
idan mutum zai sha ruwan zamzam yasha da niyya mai kyau, kuma yayi addu'a ta gari, kamar yadda magabata sukeyi,
A wani hadisin yace : Ruwan mai albarka ne, abincin mai cine, kuma ruwan mai sha ne. Muslum 2473
A wata Riwayar, Ruwa ne mai albarka, abincin mai ci, waraka daga rashin lafiya, Assunanul kubra Baihakiy, ajamiu- Sahih 2435
A wata, riwayar, Mafi alkhairin ruwa a bayan kasa shine ruwan zamzam. Sahihut-targib wat-tahib.
Nana Aishah ta kasance, tana guzirin ruwan zamzam a cikin kwalbah,
kuma tace: MANZON ALLAH SAW, yana guzirin ruwan zamzam, a cikin salka, yana zubawa, marasa lafiya, yana shayar dasu, Sahihut- tirmiziy.
Mal,Ibnul- Qayyim yace, yaga abin al'ajabi gamai da ruwan zamzam, daya gamu da rashin lafiya a maccah lokacin babu likita sai ya gwada amfani da ruwan zamzam, yana tofa suratul fatihah a ciki, ya sha ya sami lafiya. Zadul- maad.
DON ALLAH KATURAWA YAN UWANKu Na FACEBOOK KO WHATSAPP

1 comment:

  1. https://mynovels.com.ng/gidan-uncle/

    https://mynovels.com.ng/kalaman-soyayya-masu-dadi/

    https://mynovels.com.ng/hariji-hausa-novel-complete-1-and-2/

    https://mynovels.com.ng/wata-amarya-hausa-novel-complete/

    ReplyDelete